
Dalilin yasa Abba Gida-Gida zai daukaka kara
Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Kano, ya ce za su daukaka kara domin kalubalantar tabbatar da Abdullahi Umar Ganduje a matsayin zababben gwamnan jahar Kano da kotun sauraron kararrakin zabe ta yi.
Abba Kabir Yusuf ya shaida wa BBC cewa tuni lauyoyinsu suka cike dukkanin takardun da ake bukata na daukaka kara.
Mun shigar da kara domin kare hakkin al’ummar jahar Kano,
wanda suka fito kwansu da kwarkwata suka kada mana kuri’un su. in ji shi.